Gwamnatin tarayya a ranar Litinin ta ce ya zuwa wannan ranar adadin wadanda aka yiwa gwajin cutar Korona a fadin kasarnan sun kai 27,078 daga 1,127.
Dr Osagie Ehanire, ministan lafiya ne shi ne ya bayyana hakan a Abuja a yayin da yake sanar da kwamitin shugaban kasa kan lura da kuma dakile cutar Korona wato PTF.
Ehanire ya ce an samu akalla mutum 4, 399 da cutar cikin jihohi 35, inda kashi 70 na masu cutar maza ne, a yayin da kashi 30 mata ne. Inda ya ce mutum 778 suka warke daga cutar, guda 143 kuma suka rasa rayukansu.