Gwamna Dave Umahi na jihar Ebonyi ya shelanta cewa duk wani bai da lambar tantancewa ta Banki wato BVN ba zai sami albashi ba. Gwamnan ya shaidawa ma’aikatan jihar da kuma masu rike da mukaman siyasa hakan ne a ranar Laraba a garin Abakaliki a yayin da ya karbi bakuncin ma’aikatan Babban Bankin Nijeriya dake jihar, wanda shugaban Bankin na jihar Adayi Onah ya jagorance su.
Gwamnan ya ce har wala yau wannan matakin zai shafi wadanda suka ba da bayanai wadanda ba su cika ba a BVN din.
Ya ce wadanda ma ba su riga sun bude asusun Banki ba, su hanzarta su je su bude tare da BVN din.
A karshe ya jinjinawa tawagar Bankin bisa wannan ziyarar da suka kai masa, sannan ya nuna jindadinsa bisa jinjinawa gwamnatin da aka yi dangane da nasarorin da take kawo a bangarorin daban-daban.