Shugabar hukumar lura da ‘yan Nijeriya mazauna kasashe waje, NIDCOM, Mrs Abike Dabiri-Erewa, ta taya Farfesa Charles Egbu murnar ba shi mukamin jagorantar Jami’ar ‘Leeds Trinity University,’ dake East London, a kasar Birtaniya.
Dabiri-Erewa ta taya Farfesan murna ne a sakon da Jami’in hulda da jama’a na hukumar ta NIDCOM, Gabriel Odu ya fitar ya kuma rabawa manema labarai a ranar Alhamis a Abuja.
Shugabar NIDCOM din ta ce ba shi mukamin shugabantar Jami’ar da aka yi, ya nuna irin sadaukarwa da jajircewa da ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje ke yi a kasashe daban-daban na duniya.
Inda ta yi masa fatan alherin ganin ya yi amfani da kwarewarsa wajen bunkasa jami’ar da ma ilimi baki daya domin amfanar al’umma.
Farfesa Egbu ya wallafa littafai 12, tare da rubuta mukaloli fiye da 350 a Mujallu da takardu daban-daban. Kuma wannan mukamin da aka ba shi, ya kafa tarihin zama bakin fata na farko da ya samu mukamin shugabantar Jami’ar ta ‘Leeds Trinity University.’