A tsakiyar makon da muke ciki ne dai labarin wani matashi da ya kira kansa da Mala’ika ya karaɗe lungu da sakunan jihar Bauchi.
To sai dai wannan Mala’ika mai suna Musa Kurkum, ya ce kawo yanzu yan uwansa Mala’iku ba su bashi dama zuwa sama an yi mishi ɗamara don ci gaba da aikinsa na mala’ika ba.
Ko da yake wannan al’amari ya daurewa mutane da dama kai, to amma ga wannan mala’ika mai suna Musa babu wani abin tashin hankali a ciki domin ikon Allah ya wuce wasa.
Cikin tattaunawarsa da Jaridar Dimokuradiyya, wannan mala’ika ko kuma matashi Musa ya ce shi dai dan asalin Jihar Kebbi ne amma yana aikin leburanci a birnin tarayya Abuja inda nan ne yan uwansa Mala’iku suka gamu da shi suka tabbatar masa da cewa shi ma fa mala’ika ne.
Ko da yake an tambayi Musa matsayin iyayensa kan ko su ma Mala’iku ne, amma ya ce ikon Allah Ya wuce wasa don haka ya bukaci a jingine wancan tambaya don gudun shiga gonar Ubangiji.
Kazalika matashin ya ce yadda jama’a za su gaskata lamarinsa na mala’ika shine yadda Allah Ya kira sunansa tare da Annabi Ibrahim a Alkur’ani cikin Suratul A’ala.
Yanzu haka dai wannan matashi mai shekara 35 ya ce nan gaba kaɗan za a bashi dama tare da sauran Mala’iku don shi ma ya ɗaura ɗamara ya ci gaba da bauta wa Ubangiji.
To sai dai galibin jama’a na kallon wannan bawan Allah a matsayin mai taɓin hankali, yayin da a hannu guda kuma wasu ke sanya shi cikin jerin yan damfara dake fitowa a salo daban-daban a wannan zamani.
one thing which will, never end is] our. love with you, tibecause you’re the only one :in my heart.