• “Daruruwan mutane ne suka kawo mun korafe-korafen a Kan sobuwar wakar da Abdul yayi,” inji Afakallah.
• “Bansan wakar tasaba wa koyarwar addinin Musulunci ba,” inji Mawakin.
• “Ban san daya ya yi wakar ba, kuma rundunar DSS tayi abun da ya kamata,” inji Mahaifin Abdul.
Wani mawaki mai suna Ahmad Abdul da ake zargin sa da yin batanci a cikin sabuwar wakar sa, ya nemi afuwar al’umar Musulmi, gwamnatin Kano, da kuma malaman addinin Musulunci.
An dai ruwaito cewa, wakar da Abdul ya yi, ta kusan ta da yamutsi, biyo bayan martani da wasu daga cikin masu bibiyar sa suka yi, a jihar Kano.
Mawakin dai ya ce, ya yi da na sanin rera wakar, da ake takaddama a kanta.
Jaridar The Nation ta ruwaito cewa, rundunar tsaro ta farin kaya wato DSS ce, ta karkame mawakin, wanda ake ganin hakan ya tseratar da rayuwar sa, daga fishin al’uma.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yan sandan sun gurfanar da wata mata mai shekara 38 a gaban Kotu
A cewar sa, “ban ta ba sanin cewa, wakar ta sabawa koyarwar addinin Musulunci, kuma zata’iya kawo hatsaniya ba, Amma yanzu na fahimci illolin, kuma na dauki laifi na,” inji shi.
Don haka, “Ina me neman afuwar al’umar Kano, da gwamnati, da kuma hukumar kula da tace fina-finai da wakokoki,” a cewar Abdul.
A dai jiya juma’a ce, aka saki mawakin bisa wasu ka’idoji da rundunar DSS ta gindaya.
Ko da ya ke dai, hukumar kula da tace fina-finai da wakoki ta jihar, bata bayyana wakar, da ake zarkin mawakin ya yi ba.
Kazalika, sakataran hukumar Isma’il Naaba Afakallah, wanda ya ziyarci shalkwatar rundunar DSS shiyar jihar Kano inda ya ce, “na amshi daruruwan korafe-korafen al’uma, game da wakar da Abdul ya rera”.
Ya kara da cewa, “hakan yasa, na kai karar mawakin zuwa rundunar DSS, a cewar Afakallah.
A na shi bangaren, mahaifin mawakin Alhaji Abdullahi Isa, ya yaba wa rundunar tsaro ta farin kaya DSS, bisa matakin gaggawa data dauka, wanda ya kare saba wa doka da oda.
Inda a karshe ya ce, “yaron nawa ya yi wakar ce, ba tare da sani na ba”, inji Isah.