Wani masoyi a jahar Ondo, ya kone gidan surukansa bayan ya zargi budurwar sa da zubar da cikin da take dauke da shi, inda ya zargi yayarta da hura wuta tsakanin shi da masoyiyar ta sa.
mun saba samun sabani da ita kuma na kashe mata kudi da yawa Wanda har jari na bata na dubu talatin da ta rika juyawa tana saida ruwa da sauran abubuwa, bayan haka na bata ajiyar dubu Ashirin da biyar ta ajiye min, amma ta salwantar da kudin.
Kuma yayarta ma tana karbar kudi a guna kuma ita take sata tana min duk abinda taga dama har ta kaimu zuwa gun ‘yansanda.
Adedeti Williams edenuga, Wanda ake zargin kona gidan tsohuwar budurwar sa a Karamar Hukumar Okitota, da ke jahar Ondo, Ya bayyana dalilansa na daukar wanann mataki.
Budurwar mai suna Titi Sunmonu, wacce a dalilinta saurayin ya zo tsakar dare da man fetur ya shiga harabar gidan ya bude taga ya zuba a ko’ina lokacin suna bacci ya kunna wuta.
Bayan haka ya gudu ya bar garin inda a karshe bincike yasa aka kamoshi ranar litin ijobi inda yake ta yawo har aka kai ga gano shi.
Inda shelkwatar ‘Yan Sanda a akure, Inda aka masa tambayoyi kan mai yasa ya aikata hakan, Inda a karshe shariah zatayi aikin kan lamarin.