Tsohon gwamnan Kano kuma tsohon Sanatan Kano ta tsakiya Injiniya Rabiu Kwankwaso ya kira ga gwamnatin tarayya game da ƙarin farashin Man fetur.
Kwankwaso yace mafita ita ce gwamnati ta gano hanyar da kuɗaɗe ke salwanta ba wai ta ƙara farashin mai a lokacin da ake tsaka mai wuya ba.
Kwankwaso ya bayyana haka ne a yayin tattaunawarsa da sashen Hausa na BBC, a lokacin da yake ran gadin ziyarar goyon gaba ga ɗan takarar jam’iyyar PDP a jihar Edo, wato gwamna Obaseki.
Ya ce “Ƙasashe da dama a duniya a yanzu shugabanninsu na tausaya musu inda suke fito musu da tsare-tsare ta yadda zasu samu sauƙin raɗaɗin wannan annoba ta Korona, amma sai gashi a Najeriya a irin wannan yanayi sai gwamnatin tarayya ta ƙara farashin Mai”.
”A gaskiya da wuya ka samu wani wanda zai goyi bayan wannan ƙari”, kamar yadda Kwankwaso ya bayyana.
“Duk wanda ke wannan ƙasar ta san da cewa wannan ba lokaci ne na ɗorawa mutane wannan nauyi ba, don haka ma’anar hakan shi ne sabuwar yunwa da sabuwar matsalar tsaro da sabon rashin aikin yi da dai matsaloli iri-iri da zasu biyo bayan wannan mataki na gwamnatin Najeriya” a cewar Kwankwaso.
Sanata Kwankwaso ya ce idan har gwamnatin Buhari na sauraron jama’arta, to ya kamata idan ta yi abu ba dai-dai ba to ba abun kunya bane ta gyara don a samu ci gaba da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
” Ita harkar gwamnati akwai maganar kuɗin shiga akwai kuma maganar kuɗin da ake kashewa, don haka abin da ake a irin wannan yanayi shi ne sai a duba aga waɗanne ƙofofi na ɓarna za a toshe, domin akwai hanyoyi da yawa da gwamnati zata iya kawo gyara a kan irin ɓarnar da ake yi”.
Ya ce “Da irin wannan mataki gwamnati ta bi, da ‘yan ƙasa sun yi murna, sannan sun kuma ji daɗi domin kowa abin da yake so shi ne ya samu rayuwa mai inganci”.
Kwankwaso ya ce, bisa la’akari da irin arziƙin da Najeriya take dashi, ba sai an je an ɗauki wasu matakai da za su daɗa hargitsa tsarin tattalin arziƙin ƙasa ba.