Wassim Elhusseini an ayyana shi a matsayin Babban Daraktan Kamfanin Nestlé Nigeria Plc.
Elhusseini ya karbi mukamin ne daga Mauricio Alarcon wanda shi kuma aka ba shi mukamin shugaban sashen kasuwanci na Kamfanin mai lura da Yammaci da tsakiyan Afrika wanda ke dauke da kasashe 25, inda ofishinsa ke kasar Ghana.
A ranar Laraba, Victoria Uwadoka, wacce take ita ce jami’ar hulda da jama’a na Kamfanin, ta ce sabon mukamin na shi zai fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Satumba. Sai dai ta ce Alarcon zai ci gaba da zama Daraktan a kamfanin har zuwa lokacin.
A cikin watan Oktoban 2016, Alarcon ya rike mukamin Babban Daraktan Kamfanin a Nijeriya, inda kuma hukumar gudanarwar kamfanin suka bayyana jindadinsu bisa ci gaban da ya kawo wa kamfanin a yayin da ya rike mukamin.
Wassim Elhusseini, kafin ba shi sabon mukamin, Manaja ne, kuma Daraktan siye da sayarwa ne na Kamfanin Nestlé a gabas ta tsakiya da kuma Afrika ta arewa.
Elhusseini ya fara aiki ne da Nestlé a kasar Kuwait a shekarar 2002 a matsayin Manajan a bangaren CCSD. A 2015, ya koma kamfanin a gabas ta tsakiya.