Daga: Abbas Yakubu Yaura
Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta tabbatar da cewa wasu da ake zargin makiyaya ne sun kashe wasu mutanen kauyen bakwai a lokacin da suke barci a wani harin da suka kai da tsakar dare a kauyen Negga dake karamar hukumar Numan.
Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa DSP Sulaiman Nguroje ya tabbatar da kisan mutanen. Nguroje yace wasu mutane bakwai da harin ya rutsa dasu sun samu munanan raunuka a harin.
Kakakin ‘yan sandan ya kara da cewa maharan sun kaddamar da harin ne a kan al’ummar da misalin karfe 2:00 na dare ranar laraba.
’Yan sanda sun samu alamar da misalin karfe 5:00 na safe a ranar Laraba, 3 ga watan Nuwamba, an kai hari kan al’ummar Negga a karamar hukumar Numan, wani kauye da ke kan iyakar Adamawa da Taraba. A cewar rahoton farko, wadanda ake zargi da aikata laifin sun kai hari kauyen ne a lokacin da al’ummar manoma ke barci,” in ji jami’in dan sandan.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa “A yayin harin da ake kyautata zaton wasu makiyaya ne suka kai, an kashe mutane bakwai, yayin da wasu bakwai suka jikkata.”
Sannan yace rundunar ‘yan sanda ta baza runduna ta musamman a yankin yayin da wadanda suka jikkata aka kai su babban asibitin garin Numan.
Kazalika Nguroje ya yi gargadin cewa rundunar ‘yan sanda ba ta da wani hali ga kungiyoyin masu aikata laifuka dake barazana ga zaman lafiya da rayukan mutanen jihar da ba su ji ba ba su gani ba.A cewarsa, hukumar binciken manyan laifuka (CID) ta zage damtse wajen kamo maharan.
“Rundunar ‘yan sanda tana kira ga mutanen Adamawa nagari da masu son zaman lafiya dasu rika taimakawa da bayanai masu amfani don kamun kifi a tsakanin al’umma,” inji shi.