Daga Sabiu Musa.
Wasu mahara da ake zargin boko haram ne a jiya sun kashe mutum 23 a kauyen Tunga da Kabaje a yankin sakajiki dake Kauran namoda a jahar zamfara.
Mazauna yankin sunce maharan sun kai sha biyu akan babura da misalin karfe 5:30 na safe suka fara Harbin kan mai uwa dawabi inda aka kashe wasu mazauna yankin a gonakin su .
Shugaban karamar hukumar kaura namoda Alhaji Lawal Isah Abdullahi yace sunyi kokari wajen binne mamatan cikin yanayin tsaro da jami’ai.
wani mazaunin yankin mai suna Aliyu Yusha’u yace abinda ya faru da ‘Yan bijilin ko kace ‘Yan Sakai inda suke zargin wani mai a caba da cewa yana kaiwa Mahara rahoto sannan anganshi da matar shi da danshi inda kuma yake ta duba Agogo Wanda hakan yasa ake zarginsa.
an kashe shi da Wanda yake dauke da su duka sannan kuma an samu tsaro tunda naga jirgi yana ta zagaya yankin yayin da ake kokarin binne mamatan a makabarta.