Kungiyar manema labarai (Correspondents’ Chapel) da ke karkashin uwar kungiyar yan jaridu ta kasa (NUJ) reshen jihar Yobe, ta bayyana cewa ta gano take-take da barazanar da wasu mutane a jihar ke yiwa mambobin ta, inda ta bayyana cewa wannan matakin ko kadan ba zai hana ta gudanar da ayyukan ta da suka rataya wuyan ta ba- a bisa kundin tsarin mulkin Nijeriya. Bayanin hakan ya fito ne a wata takardar sanarwar manema labarai da kungiyar ta fitar- mai dauke da sa hannun sakataren ta, Ahmed A Abba (NAN), wanda ta bayyana cewa ta lura da wadannan take-taken tun bayan wani labarin da daya daga cikin mambobin ta ya rubuta, mai taken: Wasu jami’an Gaidam suna fafutikar kamun kafar zababben gwamna Buni wajen sake nada su mukamai. Wanda aka wallafa ranar 16 ga watan Mayun 2019 a jaridar ‘Daily Independent Newspaper’. Bugu da kari kuma, wannan labarin ba shida wata alaka da cin zarafi balle ko yin karan-tsaye a dokoki da ka’idojin aikin jarida, yayin da wannan barazana da wadannan mutane masu budurwar zuciyar kkadayin mulki ke yi, yana da alaka da gurguwar fassarar da suka yi wa labarin. “duk da wannan hauma-haumar da wadannan daidaikum mutanen ke yi bai dame mu ba, face kawai muna burin sauran al’umma su ankare da wannan barazanar ta hanyar kira da sakon kar ta kwana, suna yiwa marubucin wancan labarin barazana kala-kala”. “sannan yana da muhimmanci jama’a su fahimci cewa, kungiyar manema labarai a jihar Yobe, ba zata rungume hannu ta zura ido wasu mutane yan kalilan su hana ta yancin ta ba, saboda kawai yana rike da wani madafun iko ko ya hana ta aiwatar da ayyukan ta”. Inji sanarwar. Kungiyar ta kara da cewa, “wanda idan jama’a basu manta ba, yau kimanin shekara 10 da suka gabata, wannan kungiyar tana gudanar da aikin ta tare da bayar da tata gudumawa wajen samun nasarorin gwamnatin Gwamna Gaidam, amma abin bakinciki sai gashi wasu manyan jami’an wannan gamnati mai barin gado; wadanda kwadayin mulki ke neman rufe musu ido, ke kokarin amfani da wannan rahoton wajen yiwa mambobin mu barazana”. “saboda haka, muke bayyana wa karara tare da sanar da daukwacin al’umma kan cewa ba zamu yi kasa a gwiwa ba wajen aiwatar da ayyukan mu bisa yadda suke shimfide a ka’idar aikin jarida, ba tare da jin tsoro ko shakkun wani mutum ba. Kuma muna masu sanar da jami’an tsaro dangane da wannan barazana da wadannan mutane ke yi mana, kuma su sani kan cewa duk abinda ya samu daya daga cikin mambobin wannan kungiya, to yana bisan wuyan masu barazana ga yayan wannan kungiyar”. Inji shi.