By Abbas Yakubu Yaura
Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna ta tabbatar da kashe mataimakin shugaban rundunar sojin sama Muhammad Maisaka mai ritaya da wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba suka yi a gidansa dake Rigasa a karamar hukumar Igabi a Kaduna.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, Muhammad Jalige ya tabbatar da faruwar lamarin ga Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) a ranar Talata a Kaduna.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Jalige, wanda yace lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Talata, ya kuma ce mai tsaron gidan Maisaka ya samu raunuka sakamakon harin.
Sannan yace lokacin da aka samu labarin, kwamishinan ‘yan sandan, Mudassiru Abdullah ya umurci jami’in ‘yan sanda na shiyya da kwamandan yankin zuwa wurin da lamarin faru.
“An kwashe gawar zuwa asibiti sannan kuma an garzaya da mai gadin nasa zuwa asibiti domin yi masa magani,” in ji shi, yayin da ya bayyana cewa nan ba da dadewa ba za a yi cikakken bayani kan lamarin.
Jalige ya yi kira ga al’ummar Kaduna dasu fito da bayanai masu amfani kuma a kan lokaci da zasu kai ga cafke masu laifin.