JARIDAR DIMOKURADIYYA: A kalla ‘Yan banga sama da 500 ne su ka shiga Daji neman ‘yan bindiga Domin Yin Gaba da Gaba, Mafi yawan Wadanda suka an taya Dajin sun fito ne daga Yankunan Sabuwa, Faskari, Kankara, da Birnin Gwari.
Sai Dai Labarin da muke samu baya da dadin Ji domin Kuwa ‘Yan Ta’addan akalla sun kashe Mutane Sama da Sittin da Daya (61) daga yankin Sabuwa da Kankara.
Wani ganau yace a Yankin Sayau, dake Dungun Mu’azu, Sun Gano Gawarwakin Mutane Sama da Ashirin da Daya yayin da Kimanin Mutane Goma Sha Biyar kuma Sun Bata ba’a san inda suke ba.
‘Yan Ta’adan Dai suna cigaba da Korar Mutane daga Garuruwansu inda zuwa yanzu kimanin Kauyuka Goma Sha Daya ne Su ka gudu Su ka bar Garuruwan su sakamakon Ta’addancin wadannan Mutanen.
Jama’ar Garin Dungun Mu’azu, sun ce Suna Zargin Jami’an Tsaron Soja da kin daukar Matakin da ya kamata wajen tunkarar wadannan Miyagun, sun ce tsakanin wajen da Sojojin suke da inda ‘Yan ta’addan suke bai wuce kilo Mita Biyu zuwa Uku ba.
amma idan Jama’a Sun kai musu koke tareda sanar da su zuwan ‘yan ta’adan ba sa zuwa ko kuma su ce ba a ba su Umarni ba daga sama, Wanda hakan ya sa Al’umma tarar Aradu da ka, domin Tunkarar wadannan Mutanen.
A wannan Artabun Dai Ana kiyasta cewa Jama’ar Gari sun yi Nasarar Hallaka ‘Yan Ta’adda kimanin su Arba’in, inda su kuma suka kashe Mutan gari yan sa kai kimanin sittin da Daya.
Kakakin Rundunar ‘Yansandan Jahar Katsina ya tabbatar da Arangamar Sai Dai ya musanta yawan wadanda suka Rasa Rayukan nasu a Artabun, ya kuma tabbatar da cewa an Tura Runduna ta Musamman a wannan yankin domin kulawa da yankin.
Mazauna wannan yankin sun tabbatar da zuwan Jami’an tsaron tareda cewa suna nan a Garin Dandume, suna ta Harbe-Harbe cikin Gari har yanzu basu kai ga shiga cikin Dajin ba Inda nan ne Yan ta’addan su ke.