Wakulinmu shu’aibu Ibrahim Gusau
An bayyana wasu Yara su biyu, Wanda aka nemi a sakaya sunan su mazauna garin Gusau a jihar zamfara, sun maka mahaifinsu gaban kotu bisa zargin shi da zai rabasu da mahaifiyarsu.
Kamar yadda Darattan mulki na hukumar Hisba, Mal Sani Hamza kaura ya bayyanawa wakulinmu yadda abin ya faru.
Shugaban na mulki ya bayyana cewa su dai yaran su ukune babbansu ita ke da shekara Sha uku zuwa Sha hudu, sai dai mahaifiyarsu basa tare da mahaifiyarsu don sun rabu Kuma Bata Yi wani auren ba.
Ganin batada miji sai tsohon mijin nata ya Hana yaran zuwa wajanta sai lokaci bayan lokaci, sai ran nan ya kawosu su kwana biyu, ana cikin wannan halin ne sai be ganewa babban yarshiba, hakan yasa matarsa ta binciketa bincike na sosai.
Bayan wannan binciken ne aka fahinci wani ya Bata yarinyar a lokacin da take zuwa wajan mahaifiyarta, babu Wanda ya Sani hakan yasa ya dakatar da ita fita, sai bayan wani lokaci Kuma sai aka ce Masa wadannan kananan yaran daya ta bace bayan sun ziyarci mahaifiyarsu tasu.
Daga bisani sai aka fahimci cewa wannan yarta ce taje gidan mahaifirasu ta dauketa sukaje gidan wani sauri suka kwana uku.
Shugaban na mulki ya Kara da cewa daga bisani uban ya fahimci cewa itama wannan karamar yarinyar idan aka barta zata Kama haryar lalacewa, bisa wannan dalili ne uban ya hanasu fita gaba daya.
sai dai yaran sun fara kawo karane zuwa kotu daga bisani kutu ta turasu wajan ‘yansanda domin gudanar da bincike, sai dai su ‘yansanda ganin abin ya daure masu Kai , yadda za’a ce Yara ‘yanshekara biyar sun San sukai mahaifinsu kotu, to akwai dalili, sai suka tura su hukumar zisba.
Bayan hukumar hisba ta gudanar da bincike ne sai hukumar ta fahimci cewa sudai wadannan yaran shirya masu aka yi, Kuma mahaifiyarsu ta shirya masu amma ta hanasu su Fadi Wanda ya sa su, sai dai mahaifiyarsu tace masu idan aka tambayesu cewa wayasasu su kai mahaifinsu kotu suce kawar ta ce ta sasu