Rahotanni daga jamiyyar APC na nuni da cewa, Akwai masu ra’ayin cewa wasu jiga-jigan jam’iyyar APC, babu lallai su marawa takarar Tinubu baya a zaben 2023 dake tafe.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa wadanda suke daga cikin wadanda ba su ji dadin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar mai mulki, Asiwaju Bola Tinubu ba, na iya zama kan katanga ko kuma su yi masa Anti Fati a zaben 2023.
Wasu masu ruwa da tsaki na jam’iyyar sun yi kaca-kaca da tsohon gwamnan jihar Legas bayan ya lashe tikitin takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben fidda gwani na ranar 8 ga watan Yunin 2022.
KARANTA ANAN: Najeriya Na Bukatar ‘’Yanci Daga Ta’addanci Da Talauci – Sanwo-Olu
Zaku iya tunawa cewa kafin babban taron jam’iyyar na kasa, wanda ya samar da Asiwaju a matsayin dan takarar jam’iyyar APC, shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata Abdullahi Adamu ya bayyana shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC.
Sai dai kuma wasu gwamnoni da ‘ya’yan jam’iyyar da ake kyautata zaton suna biyayya ga Asiwaju ne suka dage zaben shugaban kasa a Kudu.
Hakazalika, wasu mambobin kwamitin ayyuka na kasa, NWC, sun nuna rashin amincewarsu da matakin, inda suka dage cewa sauran masu neman takarar shugaban kasa, ciki har da Asiwaju Bola Tinubu, mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo, Dr. Kayode Fayemi, dole ne a bar David Umahi da Rotimi Amaechi su tsaya takara a zaben fidda gwani.
Tinubu, wanda a karshe aka bayyana a matsayin wanda ya lashe zaben fidda gwanin, ya shaida wa Ahmad Lawan a jawabinsa na nasara a dandalin Eagles Square da ke Abuja wasu bayanai masu nuni da habaici.
Tinubu ya samu kuri’u 1,271 inda ya kayar da babban abokin hamayyarsa, Rotimi Amaechi, wanda ya samu kuri’u 316.
Wani jigo a jam’iyyar APC, Dr. Martins Apeh, wanda ya zanta da DAILY POST a Abuja ranar Asabar, ya yi ikirarin cewa a zahiri mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya ki amincewa da tayin shigar da shi cikin kwamitin yakin neman zaben shugaban kasa na jam’iyyar APC da aka saki kwanan nan.
A cewarsa, mataimakin shugaban kasa da tsohon gwamnan jihar Ribas, Rotimi Amaechi ba su da kwarin gwiwa kan takarar Tinubu kuma za su nisanta kansu daga yakin neman zabe.
A wani labarin kuma: Ranar Samun ‘Yancin Kai: Gwamna Akeredolu Ya Saki Fursunoni 16 Daga Gidan Yari
Gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu, a ranar Asabar, ya saki fursunoni 16 daga gidan yari na kasa dake Ondo.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban mai shari’a na jihar, kuma kwamishinan shari’a, wanda kuma shi ne shugaban majalisar ba da shawara ta jihar kan jinkai, Mista Charles Titiloye.
Bayanin hakan ya fito ne ta hannun babban sakataren yada labaran gwamnan, Mista Richard Olabode.