JARIDAR DIMOKURADIYYA: An gurfanar da wani shararren dan wasan gargajiya mai suna Abdur-Rasak Ahmed, a gaban babban kotun majistiri da ke zamanta a Chediya, GRA Zariya, ta jihar Kaduna, a bisa zargin lakada wa mace dukan tsiya da har ya kaita ga sumewa.
Abdur-Rasak Ahmed, dan shekaru 24 a duniya, ya shahara da sunan “Ebola” kamar yadda ake kiransa, wanda ke zaune a gida mai lamba No. 230 layin Lafiya, Kawo, ta jihar Kaduna ana tuhumarsa ne da laifin kai farmaki da kuma illata dan adam ta hanyar munanan raunuka.
Mai shigar da kara, Sajent Mansir Nasir, ya shaida wa kotun cewar Abdur-Rasak Ebola, ya lakada dukan tsitsiya ma wata mace mai suna Farida Mohammed a Gidan Dambe, Sabon Gari, a birnin Zaria a ranar 23 ga watan Mayu wacce har hakan ya kaita ga sumewa.
Sajent Nasir ya ce, ‘yan sanda sun samu labarin aukuwar lamarin, inda suka hanzarta domin kai dauki kana sun dauki Farida zuwa asibiti da karfe tara na dare, domin nemo mata lafiya.
Ya kara da cewa, Farida Muhammad ta shafe kwanaki biyu kafin ta farfado hadi da dawowa daga cikin hayyacinta.
Ya kara da cewa, wannan tuhumar kai farmaki da illata mutum ya saba wa sashi na 224 na final kod (CPC) ta jihar Kaduna.
Lauyan wanda ake kara, Gabriel Attah, ya gabatar da bukatar neman belin wanda yake karewa a gaban kotun.
Mai shari’a a babban kotun majistire, Abubakar Aliyu-Lamido ya amince da bayar da belin wanda ake zargin ne kan tsabar kudi har naira miliyan daya da kuma tabbacin wani mai dubu N500,000.
Aliyu-Lamido ya dage ci gaba da sauraron karar ne zuwa ranar 17 ga watan Afrilun 2019.