Akalla mutane bakwai ne suka mutu a lokacin da wata mummunar guguwa ta afkawa tsakiyar kasar Italiya tare da mamaye tituna da gidaje, kamar yadda hukumomi suka shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa a ranar Juma’a.
Mutane uku sun bace, ciki har da wani yaro dan shekara shida da ke tafiya a cikin mota. Kamfanin Dillancin Labarai na AGI ya ce an ceto mahaifiyar amma ruwan ya tafi da yaron.
KARANTA WANNAN LABARIN: Shirin Adashen Gata Na Aikin Hajji Yana Saukakawa — NAHCON
“A cewar karamar hukumar, adadin wadanda suka mutu na wucin gadi ya kai bakwai.
Yanzu haka an gano gawar ta bakwai,” in ji mai magana da yawun hukumar kare hakkin jama’a, yana mai tabbatar da rahotannin kafafen yada labarai na cikin gida.”
Wurin da ya fi muni shi ne Ancona, wani birni mai tashar jiragen ruwa da ke yankin Adriatic, inda yankuna da dama ba su da wutar lantarki ko wayar tarho. An rufe makarantu ranar Juma’a a yankunan da abin ya shafa.
Guguwar ta kuma afkawa makwabciyar Italiya, kasar Umbria.
Jaridar Corriere della Sera ta ce kimanin milimita 400 (inci 16) na ruwan sama ya sauka a cikin sa’o’i biyu – kusan adadin da aka saba samu a cikin watanni shida a wannan yanki.AFP
A wani labarin kuma, Gwamnatin Tarayya zata Kafa Bankunan Matasa
Ministan Matasa da Cigaban Wasanni Sunday Dare, ya ce gwamnati na shirin samar da asusun zuba jari na matasa na kasa (NYIF) don ya zama Bankunan Matasa.
Ya bayyana haka ne a ranar Alhamis yayin da yake gabatar da jawabi a taron karawa juna sani na ministoci karo na 51 da kungiyar sadarwar fadar shugaban kasa ta shirya a fadar shugaban kasa, Abuja.