Hukumar fitar da tsare-tsare da kuma taswirar gine-gine ta Kaduna wato KASUPDA ce ta dakatar da yin sallar juma’a a masallacin saboda saba dokar gini da akayi wurin ginin masallacin
An kwashi tsawon mako biyu kenan yanzu ba’a sallar juma’a a cikin masallacin
Biyo bayan hana sallar juma’a da gwamnatin jihar Kaduna ta yi a sabon masallacin Alhaji Sani Dauda wanda aka fi sani da ASD, masallacin ya dawo na yin khamsu salawat a yanzu.
Sanannen dan kasuwan nan Alhaji Sani Dauda (ASD) shi ne ya gina wannan masallaci a Yakubu Avenue dake unguwar GRA Kaduna.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, gwamnatin Kaduna ta hanyar amfani da hukumar fitar da tsare-tsare da kuma taswirar gine-gine ta Kaduna wato KASUPDA ta hana yin sallar juma’a a masallacin saboda saba dokar gini da akayi wajen gininsa.
Wakilin jaridar Daily Trust da ya samu zuwa inda masallacin yake, ya sanar da mu cewa, wannan shi ne mako na biyu kenan da ba’a gudanar da sallar juma’a ba a masallacin. A don haka jama’a suka cigaba da yin khamsu salawat kawai a cikinsa.
Wani mazaunin shiyyyar masallacin na cewa: “ Sallolin farilla guda biyar a yini kawai mu keyi a masallacin tunda aka hana yin sallar juma’a.”
Har ila yau wani makwabcin masallacin ya ce: “ Mun san da cewa gwamnati ce ta sanya dokar hana sallar juma’a a masallacin, a don haka muka maida shi na yin khamsu salawat kawai.”
Janar Manaja ta KASUPDA, Akitekt Fausat Ibikunle ta ce: “ Bamu da matsala da masallacin idan har salloli biyar na yini ake a cikinsa. Abinda ba zamu aminta ba shi ne a gudanar da sallar juma’a a wannan masallaci saboda cikin takardun izinin ginin masallacin da muka sanya ma hannu ba masallacin juma’a suka nemi zasu gina ba.”