Wakiliyarmu Zahra Sarki
An rantsar da shugabannin majalisa har biyu da mataimakansu a majalisar dokokin Jihar Bauchi, cikin ‘yan majalisu 31 da ake da su sha daya daga cikin su sun Zabi Abubakar Sulaiman, daga Mazabar Ningi, tare da Mataimakin sa Dallami Ahmad kawule, me wakiltar mazabar Zungur Galambi.
Cikin ‘yan Majalisu 11 da suka Zabi Kakakin Majalisar 9 daga Cikin su ‘Yan PDP ne daya dan jam’iyar NNPP daya kuma daga jam’iyar APC.
Wakiliyar Jaridar Dimokuradiyya, ta gano cewa A daya bangaren majalisar su ma sun gudanar da Zaben Kakakin majalisar inda suka Zabi Alhaji kawuwa Shehu Damina, daga mazabar Darazau, a matsayin Nasu kakakin Majalisar da kuma tukur Ibrahim daga Mazabar Toro, a matsayin mataimakin kakakin Majalisar.
Daya ke jawabi wa ‘yan jaridu jim kadan bayan rantsar da shi a matsayin sabon kakakin majalisa ta Tara kawuwa shehu Damina, ya bayyana cewa Zai yi kokarin ganin yakawo sauyi a tsarin dimokuradiyya a jihar Bauchi.
ya cigaba da cewa Saboda mu zamo Cikakkun mutane a matsayinmu na shuwagabanni karfe takwas saura muka shiga majalisa amma abin mamaki mun zo mun samu wasu a cikin Zauren Majalisar har mutum goma 11 kuma 9 daga Ciki ‘Yan PDP ne daya kuma Dan NNPP yayin da dayan Dan APC ne, Inji shi.
Ya kara da cewa ko da muka Tambaye su abin da ke Faruwa sai suka ce Mana Har sun yi zaben Kakakin Majalisa sun rantsar suna shirye shiryen Zaben mataimakin kakakin Majalisa ne Yanzu.
Bayan sun ganmu suka tabbatar abinda sukeyi ba gaskiya bane da suka ga basu da mafita sai suka ce sun dage Zaman majalisar Ashe duk da haka sun tafi wani gida VIP 9 inda sukaje can suka cigaba da zaben mataimakin kakakin majalisa har ma suka rantsar da shi da sauran Mambobi.
kawuwa shehu damina, yace a baya an sanya ranar litinin 17 ga watan 6 a matsayin ranar da za’a rantsar da majalisa ta Tara amma aka dage zuwa yau alhamis 20 ga wata, ba’a fara harkokin majalisa ba sai karfe 10 zuwa karfe 1 na Rana.
zaben ‘yan majalisan da akayi da sassafe yau ya fitar da Alhaji Abubakar Sulaiman a matsayin shugaban majalisa kuma an gudanar da shine karkashin kyakkyawan kulawa na isassun jami’an tsaro da suka hada da jami’an tsaro na ‘yan sanda, civil defence, da kuma jami’an farin kaya wato SSS, da kuma dakarun tsaro na soji.
Duk yunkurin da Jaridar Dimokuradiyya tayi don jin ta bakin kakakin Majalisar Abubakar Sulaiman, ya ci tura Har Zuwa lokacin da muke hada wannan rahoton kokarin mu na samunsa ta waya ya Faskara.
Sai dai jaridar Dimokuradiyya, ta gano cewa akwai wasu mambobi guda 2 daya daga mazabar Odubo, daya kuma daga mazabar Gamawa, da ke Karamar hukumar gamawa ba’a rantsar da su ba domin kuwa basu kasance suna tare da duka bangarorin guda biyu ba.