Yayin da sama da jami’an kashe gobara dubu 12 ke ta ƙoƙarin shawo kan wata wutar-daji da ke ci a California da ke Amurka, gwamnan jihar Gavin Newsom ya ce, ya nemi taimakon ƙasashen Canada da Australia, baya ga tallafin da ya nema daga gwamnatin tarayya.
Gwamnan ya ce Australia na ɗaya daga cikin ƙasashen da ke da “ƙwararrun jami’an kashe wutar-daji a duniya.”
https://dimokuradiyya.com.ng/gobarar-dajin-los-angeles-ta-sanya-an-kwashe-mutum-dubu-50/
A ranar Juma’a Newsom ya ce, wutar dajin ta yi ta’adi matuƙa a arewacin jihar, inda dubban mutane suka dinga tserewa daga gidajensu, wasu kuma ɗaruruwan gidaje da gine-gine suka kone.
A cewar Newsome, “an kwashe shekaru da dama rabon da jihar ta ga irin wannan wutar-dajin,” yana mai cewa wutar tana ƙarar da kuɗaɗe da kayayyakin da ke hannunsu.
Aƙalla mutane biyar ne suka rasa rayukansu, sannan 43 suka jikkata ciki har da jami’an kashe gobarar. Gobarar dai ta laƙume yankin da nisansa ya kai kilomita dubu 2,020.