Gwamnan jihar Zamfara Bello Matawalle ya bayyana yadda ’yan bindiga ke safarar makamai zuwa cikin Najeriya duk da cewa an rufe iyakokin ƙasar nan.
A ganawarsa da Firaministan Jamhuriyar Nijar Brigi Refini domin yaƙar ayyukan ’yan bindiga da sauran miyguan laifuka a yankin, Matawalle ya ce ’yan bindigar sun sauya salonsu na fasa-ƙwaurin makamai zuwa Neriya.
“Muna sane da cewa matsin da masu Fasa-ƙwaurin makamai a kan ababen hawa ke fuskanta ya sa yanzu sun koma amfani da raƙuma.
“Na yanke hukuncin taimakawa da motocin sintiri guda biyar baya ga ƙananan jirage marasa matuƙa da aka ba wa masu tsaron iyakar Nijar”, inji gwamnan.
Ya nuna jin daɗi da amsa kiran da Firaminista Refini ya yi, sannan ya ce Shugaban Buhari “Ya yi farin ciki da zuwanka yana kuma fatan alheri.
“Ya kuma sa in gayyace ka domin a ci gaba da taimaka wa kawo ƙarshen fashin daji a ƙasashen biyu”.
https://dimokuradiyya.com.ng/sojoji-a-jihar-zamfara-sun-yi-nasarar-cafke-yan-bindiga-50/
Gwamnan ya kuma mika masa ƙoƙon baran Shugaban ’Yan Sandan Najeriya, na cewa Jamhuriyar Nijar ta taimaka ta toshe hanyoyin safarar makamai zuwa Najeriya.
A nasa bangaren Firaministan ya nuna jin daɗinsa kan yunƙurin haɗa kai tsakanin Najeriya da ƙasarasa wajen yaƙar manyan laifuka a tsakanin iyakokin ƙasashen biyu.
Ya ƙara da cewa abun da Najeriya ke fama da shi na matsalar ’yan fashin daji da ta’addanci ba baƙo ba ne ga ƙasarasa.
Jamhuriyar Nijar ma na fama da matsaloli ta fuskoki daban-daban daga ‘Boko Haram da ’yan tayar da ƙayar baya da ga Mali da Burkina Faso.
Firaministan ya yaba ƙoƙarin gwamanman wurin kawo ƙawance da zai lalubo hanyoyin da ma dabarun magance matsalar.