Rahotanni daga jihar Adamawa sun ce ambaliyar ruwa ta mamaye akalla kauyuka 40, dake cikin kananan hukumomi 5.
Sakataren hukumar bada agajin gaggawa a Adamawan Dakta Muhd Suleiman, ya ce ibtila’in ya biyo bayan saukar ruwan sama mai yawa a wasu sassan jihar, har na tsawon kwanaki 3, inda ya ce mafi akasarin kauyukan da ambaliyar ta shafa suna gabar kogin Binuwe.
Dakta Suleiman ya ce kananan hukumomin da ambaliyar ta shafa sun hada da Girei, Numan, Fufore, Yola ta Kudu da kuma Demsa.
Sakataren hukumar bada agajin gaggawar ya kuma yi gargadin cewa, akwai yiwuwar fuskantar Karin ambaliyar, la’akari da cewar ruwan kogin na Binuwe na ci gaba da karuwa, lamarin ya haddasa yankewar hanyoyin kaiwa wasu karin kauyukan jihar ta Adamawa.