Wani jigo a jam’iyyar PDP daga jihar Akwa Ibom kuma tsohon ministan kasa, gidaje da raya birane, Nduese Essien, ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC a zaben shugaban kasa na 2023, Bola Tinubu, ba shi da wani sabon abu da zai iya samarwa da Najeriya.
A cewar sa bayan jam’iyyarsa mai mulkin kasa ta gaza cika alkawuran da ta yiwa yan kasar.
Ya ce alkawarin da Tinubu ya yi na cewa gwamnatinsa za ta sa Naira ta yi daidai da Dalar Amurka, yakin neman zabe ne kawai wanda ba zai iya tashi ba, inda ya kara da cewa mai rike da tuta na APC ba shi da irin wannan sihirin da zai juya Naira ta yi daidai da Dala, balle Tinubu.
Essien ya ce, “Tinubu ya yi irin wannan alkawari ne a shekarar 2015 lokacin da yake yi wa Muhammadu Buhari yakin neman zabe, kuma ya kasa nuna wa shugaban kasar yadda zai dawo da daraja Naira.
“Don me duk wanda ke da masaniyar yadda tattalin arzikin duniya ke aiki, zai yarda da shi?
“Haka ya faro ne a shekarar 2014, wanda ya kai ga adawa da Shugaba Goodluck Jonathan kan yadda Naira za ta kasance daidai da Dalar Amurka idan aka zabi Buhari kan mulki,” in ji Cif Essien, ya kuma kara da cewa ikirarin Tinubu ba gaskiya ba ne, idan aka yi la’akari da gaskiyar lamarin, ta yadda zai iya bin tafarkin tattalin arzikin Buhari, idan aka zabe shi a mulki.
Wa’adin dan majalisar wakilai, wanda ya jagoranci kwamitin majalisar wakilai ta kudu daga 1999 zuwa 2003, ya caccaki gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari, wadda Tinubu ke tafiya tare, saboda faduwar darajar Naira daga yadda suka same ta wato 150, inda yanzu ta koma 610 duk dala daya.
“Me yasa Tinubu ya kasa taimakawa shugaba Buhari wajen kamo faduwar Naira a kan sauran kudaden duniya amma ya jira har sai ya zama shugaban kasa a 2023 kafin ya tsoma baki ta hanyar mu’ujiza?” Essien ya tambaya.
Cif Essien ya yi kira ga ‘yan Najeriya da suka kai shekarun kada kuri’a da su yi amfani da tsawaita wa’adin da INEC ta yi na yin rajistar PVC, domin zama wani bangare na tsarin daukar shugabanni.