Shugaba Muhammadu Buhari ya rusa kwamitin dake binciken masu cin hanci da rashawa duk a kokarinta na ganin an fuskanci alkibilar yaki da cin hanci da karbar rashawa. Shugaban na daukar wannan mataki kan zargin da ake yiwa shugabannin kwamitocin da ke yaki da cin hanci da rashawa.
Buhari ya bada umurnin rushe kwamitin binciken cin hanci da rashawa da kwato dukiyoyi da kaddarorin gwamnati da aka sata nan take, wanda ke karkashin jagorancin Mista Okoi Obno Obla, wanda ake zargi da cin hanci da rashawa.
Shugaba Muhammadu Buhari ya umurci ministan shari’a kuma babban lauyan gwamnatin kasar da ya karbe ayyukan wannan kwamitin, sannan ya rusa shi, sannan ya tabbatar an kammala duk wasu bincike-bincike da aka fara ba tare da bata lokaci ba.