Kwamishinan ‘yan danda na Jihar Katsina CP Sanusi Buba, shi ne ya fito domin karbar bakuncin masu zanga-zangar lumana na nuna rashin amincewa game da kashe-kashen da ake yi a yankin Arewacin Nijeriya, lamarin da ya kare da hayaniya sakamakon kalaman Kwamishinan.
Kwamishinan bayan fitowarsa kofar gidan gwamnan jihar ya yi ma masu zanga-zangar maraba da zuwa kana ya fara da kalamansa inda ya fara da; “Babu wanda wannan al’amarin ya dame shi fiye da Shugabannin kasarnan, saboda babu wadanda suke da hakkin tsaro ya rataya a wuyansu fiye da shugabannin nan ko a wurin Allah, duk wani wanda ya fito yana nuna cewa yafi Gwamnati na kasa ko na Jiha nuna damuwa game da wannan al’amarin to wallahi karya yake yi. Inji shi
Ya ci gaba da cewa; Saboda lalurar alhakin tsaro na ko da Mutum daya ne da aka kashe ya taru ne a wuyan gwamnati, gwamnatin nan tafi kowa bakin cikin abin da ke faruwa, idan aka zo aka ce ba a taba samun matsalar tsaro fiye da na yanzu ba a baya to wallahi karya ne, sai dai in an manta, ko kuma ba a haife ku ba.
Da yake kammala jawabinsa kafin matasan su yi masa ihu, Kwamishinan ya ce, “an yi lokacin wanda jihohi 17 ‘yan ta’addah sun kwace, an yi lokacin da ba a zuwa Masallatai.”
Hakan yasa masu zanga-zangar wuka yi ta ihu suna zage-zage a wajen, idan wasu na cewa su gwamna Suka zo gani ba Kwamishinan ‘yan Sanda ba.