A Jiya Asabar ne aka buga wasan karshe a kofin zakarun nahiyar turai birnin Madrid na kasar Andulus a filin wasa na Wanda Metropolitano. Wasan an fafata shi ne tsakanin kungiyar kwallon kafa ta Liverpool da Tottenham inda Liverpool ta doke Tottenham da ci biyu da daya. Dan wasan gaba na Liverpool Mohamed Salah ne ya jefa kwallo ta farko, minti biyu da fara wasan a bugun daga kai sai mai tsaron raga kafin daga bisani Origi wanda yayi canjin Firmino ya jefa kwallo ta biyu a minti 87. Wannan shine karo na shida da Liverpool ta lashe wannan kofin bayan ta kwashe shekaru 14 rabon da ta lashe kofin.