Akalla mutane hudu da suka hada da ‘yan sanda uku ne suka mutu, sannan wasu da ba a tantance adadinsu ba suka ji rauni a lokacin da wasu da ake zargin mayakan kungiyar IS ne a yankin yammacin Afirka (ISWAP) suka kai hari a karamar hukumar Damboa ta jihar Borno, a yammacin jiya Alhamis.
Wata majiyar tsaro ta shaida wa jaridar Daily Trust cewa, yadda wasu mahara suka kai hari a sansanin jami’an yan sandan MOPOL da ke garin Damboa.
A cewar majiyar tsaron, motoci uku ne suka kone bayan da suka yi galaba a kansu kuma suka samu shiga harabar sansanin jami’an.
Ya bayyana cewa maharan sun kona jami’an Civilian JTF, da ofisoshin ‘yan banga da ke kan hanyar Biu da kuma wata motar sintiri.
KARANTA WANNAN LABARIN: Gwamna Yahaya ya Gabatar da Kasafin Kudin 2022 ga Majalisar Dokokin jihar Kogi
Majiyar ta kara da cewa harsashin ya kashe wata yarinya da ba ta da batasan hawa ba ballet sauka
“Ya zuwa yanzu mun rasa mutane hudu, ciki har da ‘yan sandan, wayar tafi da gidanka guda uku da wata yarinya da harsashi ya rutsa da ita.” Inji majiyar.
“Sun kona motoci 3 na ‘yan sanda da wata motar sintiri na ‘yan banga,” in ji majiyar.
Majiyar Jaridar Dimokudiyya ta ruwaito yadda daruruwan fararen hula suka tsere daga gidajensu a lokacin da ISWAP da jami’an tsaro suka yi musayar wuta a garin Damboa.
Hakazalika, wasu da ake zargin mayakan ISWAP ne sun kai hari a karamar hukumar Kala-Balge da ke jihar Borno a daren ranar Alhamis din da ta gabata, amma sojoji sun samu dauki cikin gaggawa.
Lamarin ya faru ne da misalin karfe 11:30 na dare a garin Rann, hedikwatar karamar hukumar Kala-Balge a jihar Borno ta tsakiya.