Mataimakin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Bishop Isaac Idahosa, a ranar Litinin, ya bayyana yadda dan takarar jam’iyyar, Rabiu Kwankwaso ya zabe shi a matsayin mataimakinsa.
Idahosa, wanda ya yi magana kai tsaye a gidan talabijin na Channels a shirin Sunrise Daily, ya ce ba shi da wani buri na tsayawa takara a siyasance a lokacin da aka bayyana shi a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa na NNPP a watan Yuli.
“Idan kana son in yi dan bayani kan yadda na shigo, a lokacin hutun Sallah, sai (Kwankwaso) ya kira ni, ‘Bishop, kana ina?” Na ce ina Legas. ‘Za ku iya zuwa Kano mu yi bikin Sallah tare?’
KARANTA KUMA Ka Rage Kudin jami’arka Ga Takawa Idan Kana Kishin Ilimi – Kwankwaso Ya Kalubalanci Atiku
“Na shigo Kano, jama’a da dama ne suka tarbe ni. Yana yin haka duk Sallah, yana ciyar da mutane. Ya ce in gaishe da mutane, kun san ina jin Hausa sosai. Ya ce, ‘Bishop, ta yaya za ka gaishe su, da Hausa ko Turanci?’ Na ce, ‘Hausa.
“Sai muka ci gaba kuma kowa ya riga ya murna. Bai taba fada min abinda ke ransa ba. Da misalin karfe 12 na daren ranar Lahadi da yamma, ya kira ni. Kimanin mako guda kenan da rufe shafin hukumar zabe ta kasa (INEC),” in ji Idahosa.
Jaridar DIMOKURADIYYA ta tattaro Bishop din ya bayyana cewa Kwankwaso, tsohon gwamnan jihar Kano, ya bayyana masa bukatar wanda zai tsaya takara daga Kudu maso Kudu, kuma ya nemi taimakonsa, wanda hakan ya sa malamin ya nemi taimakon wasu “Shugabannin addini.”
In ji Idahosa, shugabannin addinan sun tambaye shi ya “ wane shi” kuma ya ci gaba da ba da shawarwari. Sai dai ya lura cewa binciken da aka yi a ranar litinin bai yi nasara ba.
“Wanda kawai muka samu ya ce yana da iyakacin lokacin da zai iya zuwa neman shawara game da hakan. Yau talata kenan. Don haka shi (Kwankwaso) ya ce ranar Laraba, in zo gidansa da ke Maitama (Abuja) don in shiga cikin tantancewar; haka ya barshi. Ban san cewa ni ne za a tantance ba“.
A Wani Labarin Kuma Bayan Wata 8 NRC Ta Dawo Da Aiki A Titin Jirgin Kasa Daga Abuja Zuwa Kaduna
Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasa ta Kasa NRC ta dawo da aiki a hanyar jirgin Kaduna zuwa Abuja, watanni takwas bayan dakatar da jigilar.
A cikin watan Maris din da ya gabata ne mayakan Boko Haram suka kai hari kan wani jirgin kasa da ke kan hanyar, lamarin da ya yi sanadin mutuwar fasinjojin, da yin garkuwa da wasu, da kuma jikkatar fasinjojin. Hukumar NRC a sakamakon harin ta dakatar da aiki tare da neman sakin mutanen da aka sace.