A kokarin da rundunar sojojin kasar nan ke yi na yaki da ‘yan ta’adda, yanzu haka rundunar ta samu nasara cafke babban dillalin sayar da makamai a Gusau babban birnin Jihar Zamfara .
Mukaddashin jami’in yada labaru na rundunar tsaro ta kasa, Birgediya Janar Benard Onkeuko ya bayyana hakan ne a lokacin da yake tattaunawa da ‘yan Jaridu a sansanin su na hudu da ke Faskari cikin jihar Katsina .
Birgediya Janar Benerd ya bayyana cewa a ranar 22 ga watan Yuli na wannan shekara, bayan samun bayanan sirri, ga dakarun mu sun mamayi wata makaranta dake birnin Gusau , inda suka yi nasarar cafke wani dillalin makamai haifaffen qasar Nijar, mai suna Musa Abubakar wanda ake wa lakabi da Buzu.
“Dakarun sun kame Buzu tare da dan uwansa dake gadin a wannan makaranta. Bincike mu ya tabbatar mana da cewa, Buzu na shigo da makamai daga Jamhuriyyar Nijar, ta kananan Hukumomin Sabon Birni da Isa da ke Jihar Sakkwato. yanzu haka Buzu yana hannun hukumomi muna tatsar bayanai daga gareshi.” Inji Birgediya Onyeuko.
Janar Onkeuko ya kara da cewa, a ranar 25 ga watan Yuli, dakarunmu dake a Sabuwa sun sami bayanin gaggawa na garkuwa da mutane a garin, nan take dakarunmu suka bazama suka bi masu garkuwar a sansaninsu, suka tarar sun tsere sun bar wadanda suka sata har mutum hudu, suka ceto mutanen suka mayar da su ga iyalansu.
“Kuma a cikin wannan rana ta 25 ga watan Yuli, dakarunmu sun yi amfani da bayanan sirri suka afkawa maboyar ‘yan bindiga da yake Gurbin Baure cikin Jihar Zamfara a lokacin gudanar da samamen, dakarun sun hallaka mutane biyu daga cikin ‘yan bindigar da suka yi kokarin tserewa suka kuma cafke mutane uku daga cikinsu, inji Janarar Benard.
“Bugu da kari, a wannan rana dai jaruman dakarun dake kula da shiyyar Bena sun yi sintiri zuwa kauyukan Unguwar Yara, Bankami, Faduwa da Danlayi a Jihar Zamfara, inda suka yi nasarar kame wani mai baiwa ‘yan bindiga bayanai mai suna Garba Faduwa. kuma a ranar, dakarun rundunar da ke kula da shiyyar Unashi sun yi wani sintiri inda suka yi nasarar ceto wani dan bindiga suke tsare da shi mai suna Alhaji Lawal Mamman. Yanzu haka an kula da lafiyarsa a asibiti dalilin rauni da ‘yan bindiga suka ji masa.
Zaratan sojojin Nijeriya a karkashin jagorancin Operation SAHEL SANITY na ci gaba da mamayen dukkan iyakoki da lunguna domin hana duk wani dan bindiga samun wata dama ta aiwatar da mugun nufi ga al’umma.
Janar Benerd ya kara da cewa, Shugaban sojojin kasa na Najeriya, Laftanar Janar Tukur Yusuf Buratai a cikin sakonsa ga dakarun ya jinjina musu akan nasarori da suke samu ya kuma umarce su da su kara zage damtse don kawo karshen illolin da ke addabar yankin.