Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane shida, daga ciki har da matasa guda biyar wanda ‘yan uwan juna ne a yankin Gonin Gora dake karamar hukumar Chikun a jihar Kaduna.
‘Yan uwan junan wanda dukkaninsu maza ne, an yi awon gaba da su ne a yayin da suke bacci a cikin gidansu a ranar Alhamis.
Mahaifin yaran da aka yi garkuwar da su Mista Bamidele Awelewa, ya shaidawa manema labarai cewa ‘yan bidingar sun samu nasarar shigowa gidan bayan da suka fasa katangar gidan.
https://dimokuradiyya.com.ng/yan-bindiga-sun-kai-hari-tare-sa-kashe-mutane-9-a-kaduna/
Shugaban kula da harkokin tsaron cikin gida na jihar Kaduna Mista Samuel Aruwan da kuma shugaban hukumar ‘yan sanda na jihar Umar Muri, sun kaiwa iyayen yara ziyarar tare da jajanta musu.
Muri, ya tabbatarwa da mazauna yankin cewa hukumar tasu tana kokarin ganin ta kawo karshen ayyukan ta’addanci a yankin.