Ofishin hukumar yaƙi da masu yi wa Tltattalin arzikin ƙasa ta’annati (EFCC) da ke Minna, reshen jihar Neja, ya kama mutane tara da ake zargi da damfara a yanar Gizo.
Wata sanarwa da aka wallafa a shafin hukumar ta kafar sadarwar ta Facebook ta ce an kama waɗanda ake zargin ne bisa bayanin sirri da al’ummar unguwar da suke zaune suka bai wa jami’anta.
Sanarwar ta kuma ce EFCC ta kama waɗanda suka ake zargin ne a wani otal, a bayan gidan man NNPC da ke garin Minna, kan zargin yaudara ta fuskar soyayya da sauran laifukan zamba.
Ta ce abubuwan da aka karɓa daga hannun matasan masu shekaru 20 zuwa 29 sun haɗa da mota daya ƙirar Toyota Venza da na’ura mai ƙwaƙwalwa kira Laptop da kuma wayoyin hannu na alfarma.
Hukumar ta ce za ta gurfanar da su gaban kotu da zaran ta kammala binciken su.