Yajin Aiki: Taron FG, ASUU ya tashi baram-baram ba’a cimma matsaya ba
Gwamnatin Tarayya da Ƙungiyar Hada Kan Addinai a ranar Alhamis sun gaza shawo kan Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya ASUU data janye yajin aikin data ke yi, a lokacin taron da Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa Farfesa Agboola Gambari da Ministan Ƙwadago da Samar da Ayyukan yi Chris Ngige.
Taron kuma Mai Alfarma Sarkin Musulmi Sa’ad Abubakar da Shugaban Kiristoci na Najeriya Dr. Supo Ayokunle sun kasa canjawa Shuwagabannin ASUU ra’ayi akan su dawo Azuzuwa, a yayinda za’a cigaba da tattaunawa, domin biya masu haƙƙoƙin su.
KARANTA WANNAN LABARIN: Buhari ya amince da biyan Alawus na Tsaffin Sojoji
Majiyar Jaridar Dimokuraɗiyya tace an samu wani yunƙuri na Gwamnatin Tarayya da Majalisar Gamayyar Addinai na shawo kan Ƙungiyar data dawo azuzuwa a lokacin taron sirrin, suna shan alwashin cika masu alƙawurran su, amma Shuwagabancin ASUU yace dole sai Gwamnati ta biya wasu daga cikin buƙatun wanda zasu amfani dashi wajen shawo kan Mambobin ta su janye yajin aikin.
Taron dai ya wakana a ɗakin taro na Banquet dake Fadar Shugaban Ƙasa Abuja, ya samu halartar sauran Ƙungiyoyi dake da rajista a Jami’o’i, da Ƙungiyoyin Fararen Hula.
Amma daya ke bada jawabi akan abinda aka tattauna a taron, Ngige yace Gwamnatin Tarayya ta cimma matsaya da Ƙungiyar, yana mai cewa an sanya wasu sharuɗɗa, kuma wani ɓangare na yarjejeniyar da akayi za’a zartar dashi a sati mai zuwa.
A cewar Ministan, lamurran sake dubi akan Albashin su, da sake tattauanawa akan yarjejeniyar shekarar 2009 shima za’a magance shi nan bada jimawa ba.
Yace “mun cimma wasu matsaya kuma muna fatan zuwa sati mai zuwa, za’a ƙaddamar da yarjejeniyar, kuma ƙungiyoyi da dama zasu gayawa mambobin su, su janye yajin aiki.
Dayake jawabi tunda Farko, Gambari yayi kira ga Ƙungiyoyin Jami’o’i dasu sanya ra’ayin Ɗalibai a matsayin abin dubin su, yana mai cewa kuɗaɗen da suke so ba komai bane.