Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa ASUU tace har yanzu tana nan kan bakanta na ci gaba da yakin aikin da take yi yanzu haka.
Shugaban kungiyar na kasa Farfesa Emmanuel Osodeke ne ya bayyana hakan, yayin da gamayyar kungiyoyin kwadago suka shiga rana ta biyu suna zanga-zangar adawa da yajin aikin ASUU.
”baza mu janye daga yajin aikin nan ba, don shekaru biyu ma a wajen mu, ba tayi yawa ba, don haka ku ci gaba da hakuri,” Inji Osodeke.
KARANTA WANNAN LABARIN: ASUU ta bukaci yin doka kan hana yan siyasa fitar da ƴaƴansu waje don karatu
Shugaban ASUU ya kuma yabawa Kungiyar Kwadago NLC kan wannan kokari da tayi, na nuna damuwa kan halin da suke ciki.
Ya kuma bukaci daliban jami’o’in Najeriya kan su kara hakuri da matakin da kungiyar ya dauka kuwa a cewar sa sunyi hakan ne don su.
JARIDAR DIMOKURAƊIYYA ta rawaito cewa ASUU ta fara Yajin aikin ne, watanni biyar da suka wuce.