Bankin Raya Kasashen Afrika AFDB, ya ce tasirin da annobar coronavirus ke ci gaba da yi kan tattalin arzikin duniya ka iya jefa karin mutane kusan miliyan 50 cikin mummunan talauci a nahiyar Afrika.
Sabon rahoton da bankin Afrikan ya fitar wanda gidan Rediyon Faransa suka wallafa ya nuna cewa, kusan kashi 1 bisa 3 na yawan al’ummar nahiyar kwatankwacin mutane miliyan 425 aka bayyana cewa suna rayuwa kan kasa da Dala 2 a shekarar da muke ciki ta 2020, kuma yanayin ka iya munana nan gaba saboda tasirin annobar coronavirus.
Baya ga Oceania, Afrika ce nahiyar da ta fi samun saukin barnar annobar coronavirus a duniya, inda take da da kusan mutane dubu 500 da suka kamu da cutar, kuma daga cikin wannan adadin, kusan dubu 11 da 700 sun mutu, wasu akalla dubu 200 sun warke.
Sai dai matakan da gwamnatocin kasashen Afrikan suka dauke na killace jama’a da dakatar da ayyuka domin dakile yaduwar cutar, ya yi mummunan tasiri kan tattalin arzikin nahiyar ta fuskokin asarar guraben ayyukan yi da kananan sana’o’i da kuma rasa makuden kudaden shiga a tsakanin kasashe masu arzikin danyen mai da sauran ma’adanai.