Wadanda ake zargin sun kashe dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Aguata II a majalisar dokokin jihar Anambra, Okechukwu Okoye, sun bai wa masu rike da mukaman siyasa umarnin gaggawar janye sojoji daga yankin Kudu maso Gabas cikin sa’o’i 48 masu zuwa.
Wannan wa’adin yana kunshe ne a cikin wata wasika da aka samu a gefen shugaban ya kin Dan Majalissar da aka kashen.
Okoye, wanda aka yi garkuwa da shi tare da mai taimaka masa, Cyril Chiegboka, har zuwa yanzu ba a tantance wadanda suka kai harin ba a ranar 15 ga Mayu, shekarar 2022, daga bisani masu garkuwa da mutane suka sare masa kai, tare da na mataimakinsa, a kan hanya a Amichi, a ranar Asabar, inda Kuma suka yi garkuwa da su a kwanakin baya. Tare da rubutacciyar wasika
Duk da cewa ruwan sama da aka yi a wannan rana ya wanke wasu daga cikin kalmomin.
Mummunan kisan gillar da aka yi wa dan majalisar da mai taimaka masa ya haifar da fargaba da martani daga masu ruwa da tsaki a jihar.
Sai dai kwamishinan ‘yan sandan jihar, Echeng Echeng, yayin da yake kirashi domin samun cikakken bayani daga al’ummomi daban-daban domin bankado ‘yan bindigar, ya yi watsi da wannan barazanar, yana mai cewa ba “an san su ba” amma “an san su”.
Ya kuma sha alwashin gurfanar da masu aikata laifuka a jihar a gaban kotu.