Wasu ‘yan bidinga da ba a san ko su wane ba sun farwa yankin Tudu dake kauyen Agwala Dutse na karamar hukumar Kajuru a jihar Kaduna a ranar Laraba tare da kashe mutane 9.
Shugaban karamar hukumar ne Mista Cafra Caino ya tabbatarwa da manema labarai faruwar lamarin, yace daukin da jami’an soji suka kawo ne yasa ‘yan bindigar suka tsere.
Kungiyar mazauna kudancin Kaduna SOKAPU, tace akwai akalla gawar mutane 30 a cikin daji amma ba wanda ya isa yaje saboda tsoron abin zai iya faruwa.
https://dimokuradiyya.com.ng/yan-bindiga-sun-kakkabo-jirgin-yan-sanda-a-kaduna/
“A ranar Labara ne da misalin karfe 5 na safe suka farwa wannan yanki, kuma sun kashe mutane da dama tare da raunata wasu”.
Sai dai har ya zuwa yanzu da muke hada wannan rahoto, hukumar ‘yan sanda reshen jihar Kaduna bata tabbatar mana da faruwar wannan lamari ba.