Akalla manoma bakwai ne aka kashe a gonakinsu a kauyen Faru da ke karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara da sanyin safiyar Asabar.
Wani dan yankin mai suna Garba Abdullahi ya shaidawa Jaridar PUNCH cewa wadanda abin ya shafa na cikin gonakinsu ne domin girbe amfanin gona a lokacin da ‘yan bindigan suka kai musu hari suka kashe su.
Abdullahi ya bayyana cewa daya daga cikin ‘yan uwan sa Sani Akwala yana cikin manoman da ‘yan fashin suka kashe.
“Yayana, Sani Akwala na cikin wadanda wadannan ‘yan bindigar marasa Imani suka kashe ba tare da tausayi ba.”
Abdullahi ya ce ‘yan bindigar sun addabi kauyen tun farkon daminar bana.
Ya Kuma kara da cewa barayin sun sha alwashin cewa babu wani aikin noma da za a yi a yankin a lokacin daminar bana.
“‘Yan bindigar sun zagaya gonakin gonaki domin tabbatar da ana bin umarnin na su,” in ji Abdullahi.
Ya koka da cewa zai yi wuya manoma su yi noma a lokacin noman bana, yana mai kira ga hukumomin da suka dace da su gaggauta yin wani abu.
Ya bayyana fargabar cewa matukar ba a yi wani abu a kan lokaci ba, mutanen kauyen ba za su samu wani zabi illa yin hijira zuwa wasu wurare na daban ba.
“Muna shirin guduwa daga kauyen saboda kalubalen rashin tsaro da ake fama da shi domin mun fahimci cewa daga dukkan alamu ‘yan fashin ba za su bar mu mu yi noma a bana ba.”
Kokarin jin ta bakin mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, SP Mohammed Shehu, ya ci tura saboda ba a iya samunsa ta wayar tarho ba.