Rundunar ‘yan sandan Nijeriya mai yaki da ‘yan fashi ta Operation Puff Adder ta kutsa wani sansanin kungiyar ‘yan bindiga ta Ansaru, inda ta kashe 250 daga cikinsu, a cewar rundunar.
An kai harin ne a dajin Kuduru da ke Birnin Gwari a jihar Kaduna a safiyar ranar Laraba tare da taimakon sojojin sama, kuma ta ce an harbi wani jrigin helikwafta a yayin samamen.
“Samamen, wanda aka kai shi tare da hadin gwiwar rundunar IRT da ta CTU da STS da SARS, ya biyo bayan wasu bayanan sirri ne game da katafaren sansanin na Ansaru,” in ji wata sanarwa da hedikwatar ‘yan sanda ta fitar a Abuja ranar Laraba.
Ta kara da cewa: “‘Yan bindigar sun harbi wani jirgin helikwaftan ‘yan sanda, sai dai matukansa sun nuna juriya da kwarewa wurin saukar da jirgin lafiya ba tare da wani rauni babba ba.”