Wadansu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba sun kashe Benjamin Ekom, tsohon ma’ajin kudi na kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya (NUJ) reshen Nasarawa.
Ekom wanda har wala yau tsohon jami’in yada labarai ne a Masarautar Aren-Akun dake jihar, kuma kisan na shi ya zo ne mako guda da aka kashe mutum biyar a jihar.
A ranar 27 ga watan Yuli, an kashe mutum biyar a yayin da mutum 14 suka bace a kauyen Dausu dake karamar hukumar Toto na jihar.
Sarkin Aren-Akun, Alhaji Usman Galadima-Umbugadu, ya shaidawa manema labarai cewa lamarin ya auku ne a ranar Talata, inda ya bayyana kisan a matsayin wani abin bakin ciki da tir da ya auku.
Ekom, har wala yau bayanai sun nuna cewa ya rika mukamin Babban Sakatare a kungiyar ci gaban al’adun Eggon, ECDA rahotanni sun ce an kashe a ranar 3 ga watan Agusta ne a gidansa dake Washo a Akun.
Galadima-Umbugadu ya bayyana Ekom a matsayin jajirtaccen mutum wanda gudummawar da ya bai wa masarautar abu ne mai wuyar cikewa. Sarkin ya shawarci iyalin mamacin da su dauki dangana.
Da yake na shi bayanin, Hakimin Wakama, Adams Makka-Nangba, ya bayyana mutuwar Ekom a matsayin babban rashin ga masarautar Akun.
Makka-Nangba ya yi wa mamacin addu’a da nufin Allah ya jikansa.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa, Ramhan Nansel, ya shaidawa majiyarmu cewa bai samu labarin kashe Ekom din ba. Amma zai bincika domin tabbatarwa.
Bayanai sun tabbatar da cewa an kai gawar mamacin asibitin ajiye gawarwaki na Akwanga.