Mutane 7 ne suka mutu a lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai hari kauyen Naga da ke karamar hukumar Lau ta jihar Taraba a daren ranar Talata.
Majiyar Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito cewa, ‘yan bindigar sun afka garin ne a kan babura, inda sun shiga kauyen da misalin karfe 8 na dare, Kuma suka fara harbe-harbe ba kakkautawa
Kazalika Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, Yan bindigan Sun kashe mutane bakwai tare da raunata wasu da dama sanadiyar faruwar cikin lamarin.
Wata majiya a kauyen da ta nemi a sakaya sunanta, ta ce, nan da nan bayan harbe-harbe ne ‘yan bindigar suka shiga dajin.
KARANTA WANNAN LABARIN: Gwamna Badaru Na Jigawa Ya Kori Sakatarorin Kananan Hukumomin 25 a johar
Majiyar ta kuma Kara da cewa, wannan shi ne karon farko da mutanen kauyen suka fuskanci harin daga ‘yan bindiga da ba a san ko su waye ba suka kai musu.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Taraba, DSP Usman Abdullahi, ya ce, Naga inda lamarin ya faru a jihar Adamawa take, ba jihar Taraba ba..
“Yankin da lamarin ya faru (Naga) yana karkashin rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ne, ba najihar Taraba ba,” in ji DSP Abdullahi.