Wadansu ‘yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba a ranar Laraba sun kai hari a garin Agbudu dake karamar hukumar Kogi-Koton-Karfe a jihar Kogi, inda suka kashe mutum goma sha hudu tare da jikkata mutum shida.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Ede Ayuba, shi ne ya bayyana hakan a yayin ganawa da ‘yan jarida a Hedikwatar hukumar dake Lokoja, inda ya tabbatar da cewa sun samu rahoton harin da misalin karfe 2 na dare.
Ayuba ya ce mutum sha uku da ‘yan bindigar suka kashe ‘yan gida daya ne.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar ya ce bayan sun samu labarin harin, ya kira mashawarci na musamman akan harkar tsaro na karamar hukumar ta Koton-Karfe akan abin da yake faruwa, inda ya nemi da ya hada ‘yan kato da gora su je wurin kafin ‘yan sanda su je, inda ya ce ko kafin ‘yan kato da gorar su je inda ‘yan bindigar suka kai hari, har sun kammala barnarsu sun tsere.
Kwamishinan ya tabbatar da cewa yana daga cikin wadanda suka je inda aka kai harin, kuma da shi aka dauki gawarwakin wadanda aka kashe.
“Tabbas an kashe mutum 14, an yiwa mutum 6 mummunan rauni. Wani abin bakin ciki shi ne, cikin mutum 14 da aka kashe, 13 daga cikinsu ‘yan gida daya ne. A cikin gidan na su, mutum guda ne kawai ya tsira da ransa. An kashe Kawunsa, Mahaifiyarsa, Kawun matarsa, kaninsa, da matar yayansa, da matarsa da dukkanin ‘ya’yansa duk an kashe su.” ya tabbatar.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar ya ce cikin binciken da suka gudanar ya nuna cewa akwai rikicin kabilancin da aka dade ana yi a garin. Kwamishinan ya ce duk da har yanzu kisan bai nuna cewa yana da alaka da rikicin ba, amma kuma bai yi nisa da rikicin ba.
“A halin yanzu muna ci gaba da bincike. Mutum da ya tsira daga harin yana tare damu, kuma yana taimaka mana a bincikenmu. Haka Sarkin garin da wadansu manyan garin suma suna taimaka mana da bayanai.” Inji su.
Ya kara da cewa; “Ohimege na Koton-Karfe, Alhaji Abdulrazaq Isa-Koto, shima yana taimaka mana a binciken namu, haka zalika karamar hukumar da wadansu jami’an duk suna taimaka mana. Muna da tabbaci, Allah zai taimake mu, zamu gano abin da ya faru.” Ya tabbatar.
Kwamishinan ya tabbatar da cewa ba za su yi kasa a guiwa ba wajen binciken na su, tare da bankado wadanda suke da hannu a kashe-kashen.