An kashe mutum daya yayin da wasu biyu kuma aka yi garkuwa da su a wani hari da aka kai Gidan-Kwano, al’ummar da ke masaukin baki na babbar jami’ar Fasaha ta Tarayya (FUT), Minna, Jihar Neja.
Yan bindigar sun yi ta’addanci ne kai tsaye daura da babbar kofar jami’ar.
Rahotanni sun nuna cewa, lamarin ya shafi da yawa daga cikin al’ummar yankin.
Majiyoyi sun shaida wa wakilin Jaridar Daily Trust cewa, ‘yan bindigar sun kai harin ne da sanyin safiyar Alhamis.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Neja, DSP Wasiu Abiodun, ya tabbatar da faruwar lamarin, amma ya ce an shawo kan lamarin.
Sai dai ya yi shiru kan mutuwar wani mazaunin garin.
“Da misalin karfe 11:30 na dare wasu da ake zargin ‘yan bindiga ne suka kai hari wani shago a Gidan-kwano daura da kofar jami’ar FUT, inda suka yi awon gaba da yaran mai shagon.”
“Nan da nan aka tura ‘yan sanda da ‘yan banga zuwa wurin domin farautar ‘yan ta’addan, kuma a lokacin da aka bincike, an kama daya daga cikin wadanda ake zargin, kuma an kama shi a kauyen Barkuta,” in ji shi a cikin wata sanarwa.
Comments 1