A jiya ne wasu ‘yan bindiga suka kaiwa babban akanta da ke ofishin shugaban ma’aikatan Jihar Neja hari, inda suka yi awon gaba da tsabar kudi naira milyan 9.5 wanda yake dauke da su zuwa ofishin sa. An ce ‘yan bindigar sun biyo bayan babban akantan ne, Alhaji Idris Abdullahi, daga wani bankin ‘yan kasuwa har zuwa kofar shiga Sakatariyar Jihar, inda suka tsare motar na shi da wata mota marar lamba. A cewar wani ganau, ‘yan bindigar sun fara yin harbi ne ta kan mai uwa da wabi a sama, inda nan take masu ababen hawa da masu tafiya da kafa a kan babbar hanyar kowa ya yi ta gudun ceton ransa. An ce kudaden na biyan wasu aikace-aikace ne da za a yi a ofishin shugaban ma’aikatan a watan Agusta. Ganau din ya ce: ì’Yan bindigan suna tsare motar akantan, sai daya daga cikin su ya fito da sauri ya yi tsalle ya fada cikin motar da ke dauke da kudaden wadanda suke a cikin jakunkunan nan na Ghana Musta Go, ya kuma sake yin tsale ya fada cikin motar na su da tsaye tana jira tare da jakunkunan na Ghana Must Go, inda suka arce a cikin motar fijo 406 saloon karama. An ce, ‘yan bindigar wadanda suka tsere ta hanyar shatale-talen da ya yi yamma a cikin motar na su, daga baya sun sami hadari a kan hanyar na su, amma an ce sun yi nasarar kwace wata motar da suka gudu da ita. Da aka tuntubi Kakakin rundunar ‘yan sandan Jihar, DSP Muhammed Abubakar, ya tabbatar da aukuwan lamarin, yana mai cewa Jami’an rundunar sashen masu yaki da ‘yan fashi da makami sun bi bayan ‘yan fashin. A cewar shi, ìMuna biye da su, sai mun tabbatar da mun kamo su saboda mun aike da sakonni ga dukkanin wuraren da ‘yan sanda suke a cikin Jihar nan. Ya kuma ce, rundunar za ta gudanar da cikakken bincike a kan faruwar lamarin. In ba a manta ba, makwanni uku da suka shige irin hakan ta faru da ta hada da wani mai biyan kudi a sashen shari’a na Jihar, inda aka kwace naira milyan 1.9 daga hannun mai biyan kudin ta irin wannan hanyar.