A kokarinda da rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ke yi na ganin an magance matsalar tsaro a jihar Zamfara baki daya yanzu haka rundunar ‘yan sandan karkashin jagorancin Kwamishina Usman Nagogo sun karbi manyan bindigogi da kanana daga hannun Mahara da ‘Yan Sa-kai da suka addabi jihar.
Kwamishina Nagogo ya bayyana cewa ‘manyan bindigogi AK 47 guda 47, sai kuma bindigogi kirar gargajiya 200. Kuma yanzu haka Rundunar za ta ci gaba da farautar inda maharan suke don sulhu da su da karbo makamansu.
Kwamishanan ya bayyana haka ne lokacin da yake zantawa da ‘Yan jarida da kuma bayyana masu makaman a hedikwatar ‘Yan sandan da ke Gusau babban birnin jihar Zamfara. Kwamishinan ya kuma bayyana cewa sun samu gagarimar nasara ne daga gudummowar da Gwamna Bello Muhammad Matawale yake ba mu.
Kuma Rundunar ‘Yan sandan ta kama masu sanya koken a Keke Nafef suna yi wa mutane sata. Kuma yanzu haka za mu bada motocin Hilux da mai Girma gwamna Matawalen Maradun bada guda shida na hadin gwiwar jami’an tsaro na atisaye a jihar Zamfara baki daya.
Kwamishinan ya kuma tabbatar da cewa’ gamayyar jami’an tsaron za mu ci gaba da aikin ba dare babu rana don ganin an samu dawamamen zaman lafiya da kama bata-gari masu sai da miyagun kwayoyi ga matasa.