Wasu ‘yan bindiga sun sace Malamai shida a yankin tsakiyar Mali, sakamakon sun yi magana da kuma koyar da dalibai cikin harshen Faransanci.
Wani shaidar gani da ido, ya ce kafin sace Malaman, sai da ‘yan bindigar suka kona tarin litattafan dalibai a farfajiyar makarantar.
Harin na baya-bayan nan ya zo ne bayan da wata kididdiga ta nuna cewar, sama da makarantu 900 aka rufe a sassan kasar Mali, sama da kashi 2 bisa 3 daga cikinsu kuma a yankin tsakiyar kasar, saboda matsalolin tsaron da suka hada da na ta’addanci da kuma rikicin kabilanci.
A shekarar 2012 matsalar tsaro ta girmama a Mali, bayan da mayakan suka yi wa kungiyar Al-Qaeda mubaya’a suka mamaye arewacin kasar, bayan da sojojin kasar suka gaza murkushe tawayen Azbinawa.
Sai dai a shekarar 2013 dakarun Faransa suka kawo dauki, inda suka yi nasarar kwace mafi akasarin yankunan da mayakan suka mamaye.