Wakilinmu Shu’aibu Ibrahim Gusau
A daren jiya barayi sun dauke uban kasar ‘yankaba da matan sa uku a kauyen ‘yankaba da ke karamar hukumar mulkin kauran Namoda a jihar zamfara.
Barayin sun shigo garin ne cikin Daren jiya , sun Kuma sami nasaran tafiya da Matan uban kasar su uku, akwai Jummai Buhari, da Asma’u Buhari, da Lami Buhari.
Sun Kuma tafi da wani yaro Dan shekara 13 Mai suna kabiru Buhari, da wani Mai suna Sama’ila Isa, da Aminu Nakano, sun Kuma kashe wani Mai suna Sidi Abubakar.
Hon. Lawal Isah, shine shugaban karamar hukumar mulki ta kauran Namoda a zantawarsa da Wakilinmu ta wayar tafi da gidanka, ya bayyana cewa shi dai wannan kauye na ‘yankaba kauye ne da barayi Basu taba shigarsa ba sai wannan karo.
Kuma a cewarsa a halin yanzu babu kowa a garin saboda gudun ko barayin zasu dawo, Kazalika sunyi kokarin Kama wani kansila dake garin Amma ya Sami nasaran arcewa.
Sai dai ya roki hukumomin da abin ya shafa da su Kara kaimi wajan kawo karshen wannan al’amari, ya ce matukar suna cikin wannan Hali to ko Noma ba zai yiwu ba a wannan yanki.