A kalla kauyuka takwas ne a karamar hukumar Augie ta jihar Kebbi suka zama ba kowa saboda hare-haren da ‘yan bindiga suka kai musu, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na kasa NAN ya rawaito.
Kauyukan su ne Zagi, Tungar Rafi, Tungar Tudu, Keke, Kwaido, Sabongarin Kwaido, Tungar Chichira da kuma Tattazai.
Mazauna kauyukan sun yi kaura ne da yawa bayan wasu ‘yan bindiga sun kai hari Zagi a daren ranar Laraba.
Harin dai an ce ya yi sanadin mutuwar mutane uku, da dama sun jikkata, yayin da suka yi awon gaba da wasu 15.
Ambaliyar ruwa ta ruguza Al’ummomi 225 a Kano da Jigawa — NEMA
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Hakimin kauyen na Zagi, Malam Muhammadu Lawali-Sule ya ce ‘yan bindigar sun kai farmaki kauyen ne da tsakar dare.
Ya ce mutanen kauyen baki daya sun mamayi maharan amma ‘yan bindigar suka ci karfinsu.
Shugaban kauyen ya ce wadanda suka jikkata a harin na kwance a asibiti kuma suna karbar magani.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Alhaji Ahmed Magaji-Kontagora, ya ce an tattara karin jami’an tsaro zuwa yankin domin tallafa wa wadanda ke cikin garin.
Ya kuma tabbatar da cewa sojoji sun tare ‘yan bindigar tare da hana su shiga ko’ina.
Magaji-Kontagora ya shawarci mutanen da suka gudu da su koma garuruwansu su ci gaba da sana’o’insu na yau da kullum.
Ya bada tabbacin cewa za a kare rayukansu da dukiyoyinsu.
Kwamishinan ‘yan sandan ya yi kira ga jama’a da su kasance masu taka-tsan-tsan da kuma kula da harkokin tsaro, tare da tallafawa jami’an tsaro da sahihin bayanan sirri don taimakawa wajen magance matsalar rashin tsaro.
Da aka tuntubi shugaban karamar hukumar Augie, Alhaji Lawal Muhammad ta wayar tarho, ya ce an tsaurara matakan tsaro a kewayen kauyukan da sauran yankunan.
Ya kara da cewa an kafa sansanin ‘yan gudun hijira a yankin.
“Dole ne mu yabawa jami’an tsaro a jihar kan yadda suka tura jami’an tsaro domin dakile sake afkuwar lamarin.
“Ba tare da bata lokaci ba jami’an tsaro sun mayar da martani ta hanyar tura karin jami’ai, kuma yanzu haka al’amura sun dawo yankin.
“Ina so in yi kira ga mutanen da suka bar al’ummarsu da su kasance masu hakuri da natsuwa.
“An kafa sansanin ‘yan gudun hijira a wata makaranta da ke yankin.
“Gwamnati da jami’an tsaro suna yin iyakacin kokarinsu domin suna sane da halin da suke ciki kuma za su yi duk mai yiwuwa da mutum zai iya wajen kare rayukansu da dukiyoyinsu,” in ji shugaban.
(NAN)