An yi garkuwa da wasu jiga-jigan jam’iyyar APC mai mulki a jihar Kaduna a wani hari da aka kai a hanyar Kaduna zuwa Kachia a jihar Kaduna.
Jaridar Dimokuraɗiyya ta rawaito cewa harin ya faru ne a wani wuri mai suna Tashar Icce, wanda ke da tazarar wasu mitoci daga al’ummar Kujama da ke yankin Kajuru a jihar.
Tawagar ta na kan hanyarta ta dawowa ne daga Kafanchan bayan wata ganawar siyasa da shugabannin addinin Kirista a gundumar Sanata ta Kudu, ranar Alhamis.
KARANTA ANAN: Wike: Abinda Atiku Ya Yi Min Alkawari A Landan
Wani dan siyasa da ya tsallake rijiya da baya, ya bayyana lamarin a matsayin mai muni, inda ya ce kimanin motoci biyar ne abin ya shafa.
Ya ce ‘yan bindigar sun bude wuta ne kai tsaye, kuma wasu daga cikin mutanen da ke cikin tawagar sun samu raunuka da bindiga yayin da aka yi garkuwa da mutane biyu.
Dimokuradiyya ta kuma gano cewa dan takarar gwamna, Sanata Uba Sani, baya cikin tawagar da aka kai wa harin yayin da ya taso daga Kafanchan zuwa Abuja.
Shugaban yakin neman zaben sa, Sani Maina, Ahmed Maiyaki, jigo a jam’iyyar, da wasu sun tsallake rijiya da baya a yayin harin.
Daga cikin wadanda aka sace akwai dan takarar majalisar wakilai na jam’iyyar APC a Kajuru Mista Madaki da mataimakin shugaban jam’iyyar APC na karamar hukumar Kajuru, Ruben Waziri.
A wani labarin kuma: Tsaftar Muhalli: Mun Tanadi Kotunan Tafi Da Gidan Ka Ga Masu Kunnen Kashi – Kabiru Getso
Ma’aikatar muhalli ta jihar Kano ta ce shirye shirye sun kammala domin ganin an gudanar da tsaftar muhalli ta karshen wata da aka saba gudanar da ita a duka ranar asabar din karshen wata.
Daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar Ismail Garba Gwammaja ne ya bayyana haka a ganawarsa da manema labarai, yana bukatar alumma da su bayar da hadin kai wajen zama a gida tare da tsaftace muhallansu, daga karfe 7 zuwa 10 na safe.