By Abbas Yakubu Yaura
Rahotanni sun bayyana cewa ana zargin an yi garkuwa da mutane 8 a ranar Talata a Itapaji-Ekiti mako guda bayan an yi garkuwa da mutane hudu a Ayebode-Ekiti dake karamar hukumar Ikole a jihar Ekiti.
Sai dai an ce wadanda suka yi garkuwa da su sun tuntubi iyalan wadanda abin ya shafa a ranar Laraba inda suka bukaci a biya su kudi Naira miliyan 50 a matsayin kudin fansa.
Wani shaidan gani da ido ya bayyanawa manema labarai a Ado-Ekiti, babban birnin jihar a ranar Larabar da ta gabata, cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki wani gida dake garin da misalin karfe 9:30 na dare, inda suka yi ta harbe-harbe akan iska tare da yin awon gaba da mutane takwas dake cikin ginin.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa An kwashe sama da sa’a guda ana harbe-harbe a cikin jama’ar yankin.
Majiyar ta ce mai gidan yana shirye-shiryen gudanar da binne mahaifiyarsa kuma alokacin shirye-shiryen mugayen suka kai hari.“Mutanen su bakwai sun zo ne da misalin karfe 9:30 na dare dauke da bindigogi suka kewaye ginin.inda suka yi ta harbe-harbe ba kakkautawa.
“A lokacin da mutanen gidan ke fitowa, sai aka kama su, suka kwanta. Daga baya aka tafi da su cikin daji. Tun farko su 14 ne, amma shida daga cikinsu sun tsere cikin daji”.
Da aka tuntubi jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ekiti, Sunday Abutu, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Kazalika Abutu ya ce: “Rundunar tana aiki akan hakan. Tuni aka tura jami’an ‘yan sanda na musamman da kuma JTF a cikin wannan sashe domin tabbatar da ceto wadanda abin ya shafa da kuma yiyuwar cafke masu laifin”.