By Abbas Yakubu Yaura
Hukumar tsaro ta farin kaya ta Najeriya NSCDC ta tabbatar da cewa wasu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kai hari kauyen Nuku dake karamar hukumar Kaiama ta jihar Kwara.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun mai magana da yawun rundunar ta jihar Kwara, Mista Babawale Afolabi, kuma aka rabawa manema labarai a Ilorin ranar Alhamis.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa ‘yan bindigar sun yi awon gaba da wasu yara kanana biyu ‘yan gida daya tare da raunata mai gidan da wani mutum guda da adduna,inda daga baya aka sako ‘yan matan da aka sace bayan da masu garkuwan suka yi musu fyade.
“Da sanyin safiyar ranar 3 ga watan Nuwamba, wasu ‘yan bindiga da har yanzu ba a tantance ko su wanene ba sun kai hari a matsugunin Alhaji Hassan Yunusa, a kauyen Nuku dake Kaiama.“Bincike ya nuna cewa maharan da gaske suna neman kudi ne, saboda suyi awon gaba da wani a wurin amma ba su ga komai ba.
“Sun far wa Alhaji Yunusa da kuma wani mai suna Woru Yunusa da raunukan adduna da dama sannan suka tafi tare da ‘yan mata biyu, amma daga baya ‘yan sa’o’i kadan suka sako su.
“An gano cewa wadanda suka sace ‘yan matan sunyi musu fyade wadanda basu ji ba su gani ba,” inji shi.
Kakakin yace mutanen biyu da aka farmaka suna karbar magani a wani wurin jinya kuma an yi musu gwajin lafiya.